1. “Ku ji wannan, ya ku firistoci!Ku saurara, ya mutanen Isra'ila!Ku kasa kunne, ya gidan sarki!Gama za a yi muku hukunci,Domin kun zama tarko a Mizfa,Da ragar da aka shimfiɗa a bisa Tabor.
2. Sun tayar, sun yi zurfi cikin zunubi,Zan hore su duka.
3. Na san Ifraimu, Isra'ila kuma ba a ɓoye take a gare ni ba.Gama Ifraimu ta yi aikin karuwanci,Isra'ila kuma ta ƙazantu.