Yush 12:7-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Ubangiji ya ce, “Ɗan kasuwa wanda yake da ma'aunin algus a hannunsa.Yana jin daɗin yin zalunci.

8. Mutanen Ifraimu sun ce, ‘Hakika, mun zama attajirai,Mun samar wa kanmu dukiya.A cikin harkokinmu ba za a sami wata mugunta ba.’

9. Ni ne Ubangiji Allahnku tun daga ƙasar Masar,Zan kuma sa ku zauna cikin alfarwai,Kamar lokatan ƙayyadaddun idodi.

10. “Na yi magana da annabawa,Ni ne na ba da wahayi da yawa,Da misalai kuma ta wurin annabawa.

Yush 12