Yush 11:5-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. “Ba su koma ƙasar Masar ba,Amma Assuriya za ta zama sarkinsuGama sun ƙi yarda su koma wurina.

6. Takobi zai ragargaje biranensu,Zai lalatar da sandunan ƙarafan ƙofofinsu,Zai cinye su domin muguwar shawararsu.

7. Mutanena sun himmantu su rabu da ni,Ko da yake an kira su ga Ubangiji,Ba wanda ya girmama shi.

8. “Ƙaƙa zan iya rabuwa da ke, ya Ifraimu?Ƙaƙa zan miƙa ki, ya Isra'ila?Ƙaƙa zan maishe ki kamar Adma?Ƙaƙa zan yi da ke kamar Zeboyim?Zuciyata tana motsawa a cikina,Juyayina ya huru.

Yush 11