Yah 8:15-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Ku kuna hukunci irin na duniya ne, ni kuwa ba na hukunta kowa.

16. Amma ko da zan yi hukunci, hukuncina na gaskiya ne, domin ba ni kaɗai nake ba, ni da Uba wanda ya aiko ni ne.

17. A Attaurarku ma a rubuce yake, cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.

18. Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”

19. Saboda haka suka ce masa, “Ina Uban naka yake?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko ni ko Ubana, ba wanda kuka sani. Da kun san ni, da kun san Ubana ma.”

Yah 8