Yah 6:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Bayan haka Yesu ya haye Tekun Galili, wato Tekun Tibariya.

2. Sai taro mai yawa suka bi shi, don sun ga mu'ujizan da yake yi ga marasa lafiya.

3. Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.

4. To, Idin Ƙetarewa, wato idin Yahudawa, ya gabato.

5. Da Yesu ya ɗaga kai ya hango babban taro yana doso shi, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayo gurasar da mutanen nan za su ci?”

Yah 6