6. Abin da mutum ya haifa mutum ne, abin kuma da Ruhu ya haifa ruhu ne.
7. Kada ka yi mamaki domin na ce maka, ‘Dole a sāke haifarku.’
8. Iska tana busawa inda ta ga dama. Kakan ji motsinta, amma ba ka san inda ta fito da inda za ta. Haka fa yake ga duk wanda Ruhu ya haifa.”
9. Sai Nikodimu ya amsa masa ya ce, “Ƙaƙa wannan zai yiwu?”