7. Sai almajirin nan da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ubangiji ne dai!” Da Bitrus ya ji, ashe, Ubangiji ne ya yi ɗamara da taguwarsa, don a tuɓe yake, ya fāɗa tekun.
8. Sauran almajirai kuwa suka zo a cikin ƙaramin jirgi, janye da tarun cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, kamar misalin kamu ɗari biyu ne.
9. Da fitowarsu gaci sai suka ga garwashi a wurin, da kifi kai, da kuma gurasa.
10. Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifi a na waɗanda kuka kama yanzu.”