Yah 2:2-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. aka kuma gayyaci Yesu da almajiransa.

3. Da ruwan inabi ya gaza, uwar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”

4. Yesu ya ce mata, “Iya, ai, wannan magana ba taki ba ce. Lokacina bai yi ba tukuna.”

5. Sai uwa tasa ta ce wa barorin, “Duk abin da ya ce ku yi, sai ku yi.”

6. A wurin kuwa akwai randuna shida na dutse a ajijjiye, bisa ga al'adar Yahudawa ta tsarkakewa, kowacce na cin wajen tulu shida shida.

7. Sai Yesu ya ce musu, “Ku cika randunan nan da ruwa.” Suka ciccika su fal.

Yah 2