1. A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta ƙasar Galili. Uwar Yesu kuwa tana nan,
2. aka kuma gayyaci Yesu da almajiransa.
3. Da ruwan inabi ya gaza, uwar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”
4. Yesu ya ce mata, “Iya, ai, wannan magana ba taki ba ce. Lokacina bai yi ba tukuna.”
5. Sai uwa tasa ta ce wa barorin, “Duk abin da ya ce ku yi, sai ku yi.”