W. Yah 16:6-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Don mutane sun zub da jinin tsarkaka da na annabawa,Ga shi kuwa, ka ba su jini su sha.Sakamakonsu ke nan!”

7. Sai na ji wata murya a bagadin ƙona turare, tana cewa,“Hakika, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki,Hukuncinka daidai yake, na adalci ne kuma!”

8. Sai mala'ika na huɗu ya juye abin da yake a tasarsa a rana, sai aka yardar mata ta ƙona mutane da wuta.

9. Sai matsanancin zafi ya ƙona mutane, har suka zagi sunan Allah, shi da yake da ikon waɗannan bala'i, ba su kuwa tuba sun ɗaukaka shi ba.

W. Yah 16