Rom 9:14-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. To, me kuma za mu ce? Allah ya yi rashin adalci ke nan? a'a, ko kusa!

15. Domin ya ce wa Musa, “Wanda zan yi wa jinƙai, zan yi masa jinƙan, wanda zan nuna wa tausayi kuwa, zan nuna masa tausayin.”

16. Ashe kuwa, abin bai danganta ga nufin mutum ko himma tasa ba, sai dai ga jinƙan Allah.

17. Don a Nassi an ce da Fir'auna, “Na girmama ka ne musamman, domin in nuna ikona a kanka, domin kuma a sanar da sunana a duniya duka.”

18. Wato, yana nuna jinƙai ga wanda ya so, yana kuma taurara zuciyar wanda ya so.

19. Kila ka ce mini, “To, don me har yanzu yake ganin laifi? Wa zai iya tsayayya da nufinsa?”

Rom 9