Neh 9:22-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. “Ka sa sun ci al'ummai da mulkoki da yaƙi,Ƙasashen da suke maƙwabtaka da tasu.Suka ci ƙasar Sihon, Sarkin Heshbon,Da ƙasar Bashan, inda Og yake sarki.

23. Ka riɓaɓɓanya zuriyarsu kamar taurarin sararin sama,Ka sa suka ci ƙasar, suka zauna cikinta,Ƙasar da aka yi wa kakanninsu alkawari za ka ba su.

24. Saboda haka zuriyarsu suka shiga, suka mallaki ƙasar Kan'ana.Ka rinjayi mutanen da suke zama a can.Ka ba jama'arka iko su yi yadda suke soDa mutane, da sarakunan ƙasar Kan'ana.

25. Sun ci birane masu garu, da ƙasa mai dausayi,Da gidaje cike da dukiya, da rijiyoyi, da gonakin inabi,Da itatuwan zaitun, da itatuwa masu 'ya'ya.Suka ci dukan abin da suke so, suka yi taiɓa,Suka mori dukan kyawawan abubuwan da ka ba su.

26. “Amma suka yi maka rashin biyayya, suka tayar maka,Suka juya wa dokokinka baya,Suka karkashe anna bawan da suka faɗakar da su,Waɗanda suka faɗa musu su juyo gare ka.Suka yi ta saɓa maka lokaci lokaci.

Neh 9