1. Taku ta ƙare, ku masu shiryamugunta,Masu tsara mugunta a gadajensu!Sa'ad da gari ya waye, sai su aikatata,Domin ikon aikatawa yanahannunsu.
2. Sukan yi ƙyashin gonaki da gidaje,sai su ƙwace.Sukan zalunci mutum, su ƙwacegidansa da gādonsa.
3. Domin haka Ubangiji ya ce,Ga shi, yana shirya wa wannanjama'a masifa,Wadda ba za ku iya kuɓuta dagacikinta ba.Ba kuma za ku yi tafiyar alfarma ba,Gama mugun lokaci ne.
4. A wannan rana za su yi karinmagana a kanku,Za su yi kuka da baƙin ciki maizafi,Su ce, “An lalatar da mu sarai!Ya sāke rabon mutanena,Ya kawar da shi daga gare ni!Ya ba da gonakinmu ga waɗandasuka ci mu da yaƙi.”
5. Don haka ba za ku sami wanda zai samuku ma'auniA taron jama'ar Ubangiji ba.
6. “Kada su yi wa'azi,” amma sun yiwa'azi.“Idan ba su yi wa'azi a kanabubuwan nan ba,Raini ba zai ƙare ba.
7. Daidai ne a faɗi haka, ya jama'arYakubu?‘Ruhun Ubangiji ya yi rashin haƙurine?Waɗannan ayyukansa ne?’ ”“Ashe, maganata ba takan amfanawanda yake tafiya daidai ba?”
8. Ubangiji ya amsa ya ce,“Ba da daɗewa ba mutanena suntashi kamar maƙiyi,Kukan tuɓe rigar masu wucewa dasalama, masu komawa da yaƙi.
9. Kukan kori matan mutanenaDaga gidajensu masu kyau,Kukan kawar da darajata har abadadaga wurin 'ya'yansu.