15. Sai suka karɓi kuɗin, suka yi yadda aka koya musu. Wannan magana kuwa, ta bazu cikin Yahudawa har ya zuwa yau.
16. To, almajirai goma sha ɗayan nan suka tafi ƙasar Galili, suka je dutsen da Yesu ya umarce su.
17. Da suka gan shi, suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka.
18. Sai Yesu ya matso, ya ce musu, “An mallaka mini dukkan iko a Sama da ƙasa.
19. Don haka sai ku je ku almajirtar da dukkan al'ummai, kuna yi musu baftisma da sunan Uba, da Ɗa, da Ruhu Mai Tsarki,