Mat 27:35-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

35. Da suka gicciye shi, suka rarraba tufafinsa a junansu ta jefa kuri'a.

36. Suka zauna a nan suna tsaronsa.

37. A daidai kansa aka kafa sanarwar laifinsa cewa, “Wannan shi ne Yesu, Sarkin Yahudawa.”

38. Sai kuma aka gicciye 'yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a dama, ɗaya a hagun.

Mat 27