35. Da suka gicciye shi, suka rarraba tufafinsa a junansu ta jefa kuri'a.
36. Suka zauna a nan suna tsaronsa.
37. A daidai kansa aka kafa sanarwar laifinsa cewa, “Wannan shi ne Yesu, Sarkin Yahudawa.”
38. Sai kuma aka gicciye 'yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a dama, ɗaya a hagun.