5. Amma suka ce, “Ba dai a lokacin idi ba, don kada jama'a su yi hargitsi.”
6. To, sa'ad da Yesu yake Betanya a gidan Saminu kuturu,
7. sai wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tandu na man ƙanshi mai tsadar gaske, ta tsiyaye masa a kā, a lokacin da yake cin abinci.
8. Amma da almajiran suka ga haka, sai suka ji haushi suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!