43. Har yanzu dai ya dawo ya ga suna barci, don duk barci ya cika musu ido.
44. Har wa yau ya sāke barinsu, ya koma ya yi addu'a ta uku, yana maimaita maganar dā.
45. Sai ya komo wurin almajiran, ya ce musu, “Har yanzu barci kuke yi, kuna hutawa? To, ga shi, lokaci ya yi kusa. An ba da Ɗan Mutum ga masu zunubi.
46. Ku tashi mu tafi. Kun ga, ga mai bashe ni nan, ya matso!”