10. Yesu kuwa da ya lura da haka, sai ya ce musu, “Don me kuke damun matar nan? Ai, alheri ta yi mini, na gaske kuwa.
11. Kullum kuna tare da talakawa, amma ba kullum ne kuke tare da ni ba.
12. Zuba man nan da ta yi a jikina, ta yi shi ne domin tanadin jana'izata.
13. Hakika, ina gaya muku, duk inda za a yi bisharar nan a duniya duka, abin da matar nan ta yi za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
14. Sai ɗaya daga cikin sha biyun nan, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya je wurin manyan firistoci,