18. “An ji wata murya a Rama,Ta kuka da baƙin ciki mai zafi,Rahila ce take kuka saboda 'ya'yanta.Ba za ta ta'azantu ba, don ba su.”
19. Amma bayan mutuwar Hirudus, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki a Masar, ya ce,
20. “Tashi ka ɗauki ɗan yaron da uwa tasa, ka tafi ƙasar Isra'ila, don masu neman ran ɗan yaron sun mutu.”