Mat 16:20-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Sai ya kwaɓi almajiransa ƙwarai kada su gaya wa kowa shi ne Almasihu.

21. Tun daga lokacin nan Yesu ya fara bayyana wa almajiransa, lalle ne ya tafi Urushalima, ya sha wuya iri iri a hannun shugabanni da manyan firistoci da malaman Attaura, har a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.

22. Sai Bitrus ya ja shi waje ɗaya, ya fara tsawata masa, ya ce, “Allah ya sawwaƙe, ya Ubangiji! Wannan har abada ba zai same ka ba!”

Mat 16