1. Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo suka roƙe shi ya nuna musu wata alama daga Sama, domin su gwada shi.
2. Ya amsa musu ya ce, “In magariba ta yi, kuka ga sama ta yi ja, kukan ce, ‘Aha, gari zai yi sarari.’
3. Da safe kuma in kun ga sama ta yi ja, ta kuma gama gari, kukan ce, ‘Yau kam, za a yi hadiri.’ Kuna iya gane yanayin sararin sama, amma ba kwa iya gane alamun zamanin nan.
4. 'Yan zamani, mugaye, maciya amana, suke nema su ga wata alama, amma ba wata alamar da za a nuna musu, sai dai ta Yunusa.” Sai ya bar su ya tafi.
5. Da almajiran suka isa wancan ƙetare, ashe, sun manta ba su kawo gurasa ba.