51. “Kun fahimci duk wannan?” Suka ce masa, “I.”
52. Sai ya ce musu, “To, duk malamin Attaura da ya zama almajirin Mulkin Sama, kamar maigida yake, wanda ya ɗebo dukiya sabuwa da tsohuwa daga taskarsa.”
53. Da Yesu ya gama waɗannan misalai, sai ya tashi daga nan.