5. Sai waɗanda suke tsaitsaye a gun suka ce musu, “Don me kuke kwance aholakin nan?”
6. Suka faɗa musu abin da Yesu ya ce. Su kuwa suka ƙyale su suka tafi.
7. Suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfiɗa mayafansu a kai, ya hau.
8. Sai mutane da yawa suka shisshimfiɗa mayafansu a hanya, waɗansu kuma suka baza ganyen da suka kakkaryo a saura.