20. Suna wucewa da safe, sai suka ga ɓauren nan ya bushe har saiwarsa.
21. Bitrus kuwa ya tuna, sai ya ce masa, “Ya Shugaba, dubi! Ɓauren nan da ka la'anta ya bushe!”
22. Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku gaskata da Allah.
23. Hakika, ina gaya muku, kowa ya ce wa dutsen nan, ‘Ka ciru, ka faɗa teku’, bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata abin da ya faɗa zai auku, sai a yi masa shi.