1. Farkon bisharar Yesu Almasihu, Ɗan Allah, ke nan.
2. Yadda yake a rubuce a littafin Annabi Ishaya cewa,“Ga shi, na aiko manzona ya riga ka gaba,Wanda zai shirya maka hanya.
3. Muryar mai kira a jeji tana cewa,Ku shirya wa Ubangiji tarfarki,Ku miƙe hanyoyinsa.”
4. Yahaya Maibaftisma ya bayyana a jeji, yana wa'azi mutane su tuba a yi musu baftisma domin a gafarta musu zunubansu.
5. Sai duk mutanen ƙasar Yahudiya, da dukan mutanen Urushalima suka yi ta zuwa wurinsa, suna bayyana zunabansu, yana yi musu baftisma a Kogin Urdun.