9. Gara ma waɗanda takobi ya kasheDa waɗanda yunwa ta kashe,Gama sun rame sarai saboda rashin abinci.
10. Mata masu juyayi, da hannuwansuSuka ɗauki 'ya'yansu, suka dafa,Suka zama musu abinci a lokacin halakar mutanena.
11. Ubangiji ya saki fushinsa,Ya zuba fushinsa mai zafi.Ya kunna wa Sihiyona wutaWadda ta cinye harsashin gininta.
12. Sarakunan duniya da mazaunanta ba su gaskata,Cewa abokan gaba ko maƙiyaZa su iya shiga ƙofofin Urushalima ba.
13. Dalili kuwa saboda zunuban annabawa ne,Da muguntar firistoci,Waɗanda suka kashe adalai.
14. Sun yi ta kai da kawowa a titi kamar makafi,Sun ƙazantu da jiniHar ba wanda zai taɓa rigunansu.
15. Mutane suka yi ta yi musu ihu,Suna cewa, “Ku tafi, ku ƙazamai,Ku tafi, ku tafi, kada ku taɓa mu!”Don haka suka zama korarru, masu kai da kawowa.A cikin sauran al'umma mutane suna cewa,“Ba za su ƙara zama tare da mu ba.”
16. Ubangiji kansa ya watsar da su,Ba zai ƙara kulawa da su ba.Ba su darajanta firistoci ba,Ba su kuma kula da dattawa ba.
17. Idanunmu sun gajiDa zuba ido a banza don samun taimako,Mun zuba idoGa al'ummar da ba za ta iya cetonmu ba.