54. Ruwa ya sha kaina,Sai na ce, ‘Na halaka.’
55. “Ya Ubangiji, na yi kira ga sunankaDaga cikin rami mai zurfi.
56. Ka kuwa ji muryata.Kada ka rufe kunnenka ga jin kukana na neman taimako.
57. Sa'ad da na yi kira gare ka, ka zo kusa.Sa'an nan ka ce mini kada in ji tsoro.
58. “Ka karɓi da'awata, ya Ubangiji,Ka kuwa fanshi raina.