Mak 3:43-60 Littafi Mai Tsarki (HAU)

43. “Ka yafa fushi, ka runtume mu,Kana karkashe mu ba tausayi.

44. Ka kuma rufe kanka da gajimareDon kada addu'a ta kai wurinka.

45. Ka maishe mu shara da juji a cikin mutane.

46. “Dukan maƙiyanmu suna yi mana ba'a.

47. Tsoro, da wushefe,Da lalatarwa, da hallakarwa sun auka mana.

48. Hawaye suna gangarawa daga idanuna kamar ruwan koguna,Saboda an hallaka mutanena.

49. “Hawayena suna ta gangarawa, ba tsayawa, ba hutawa,

50. Har lokacin da Ubangiji daga Sama ya duba, ya gani.

51. Ganin azabar 'yan matan birninaYa sa ni baƙin ciki.

52. “Waɗanda suke maƙiyana ba daliliSun farauce ni kamar tsuntsu.

53. Sun jefa ni da rai a cikin rami,Suka rufe ni da duwatsu.

54. Ruwa ya sha kaina,Sai na ce, ‘Na halaka.’

55. “Ya Ubangiji, na yi kira ga sunankaDaga cikin rami mai zurfi.

56. Ka kuwa ji muryata.Kada ka rufe kunnenka ga jin kukana na neman taimako.

57. Sa'ad da na yi kira gare ka, ka zo kusa.Sa'an nan ka ce mini kada in ji tsoro.

58. “Ka karɓi da'awata, ya Ubangiji,Ka kuwa fanshi raina.

59. Ka ga laifin da aka yi mini,Sai ka shara'anta da'awata, ya Ubangiji.

60. Ka ga dukan irin sakayyarsu,Da dukan dabarun da suke yi mini.

Mak 3