Mak 3:14-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Na zama abin dariya ga dukan mutane,Dukan yini suna yi mini waƙar zambo.

15. Ya shayar da ni da ruwan ɗaci,Ya ƙosar da ni da abinci mai ɗaci.

16. Ya sa in tauna tsakuwa da haƙorana,Ya zaunar da ni cikin ƙura.

17. An raba ni da salama,Na manta da abar da ake ce da ita wadata.

18. Sai na ce, “Darajata ta ƙare,Ba ni kuma da sa zuciya wurin Ubangiji.”

Mak 3