Mak 3:10-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Ya zamar mini kamar beyar wanda yake fako,Kamar zaki a ɓoye cikin ruƙuƙi.

11. Ya bauɗar da ni daga hanyata, ya yayyage ni,Ya maishe ni, ba ni a kowa.

12. Ya ja bakansa, ya sa in zama abin baratarsa.

13. Ya harbe zuciyata da kiban kwarinsa.

14. Na zama abin dariya ga dukan mutane,Dukan yini suna yi mini waƙar zambo.

15. Ya shayar da ni da ruwan ɗaci,Ya ƙosar da ni da abinci mai ɗaci.

16. Ya sa in tauna tsakuwa da haƙorana,Ya zaunar da ni cikin ƙura.

17. An raba ni da salama,Na manta da abar da ake ce da ita wadata.

18. Sai na ce, “Darajata ta ƙare,Ba ni kuma da sa zuciya wurin Ubangiji.”

19. Ka tuna da azabata, da galabaitata,Da ɗacin raina, da kumallon da nake fama da shi.

20. Kullum raina yana tunanin azabaina,Raina kuwa ya karai.

21. Da na tuna da wannan, sai na sa zuciya ga gaba.

22. Ƙaunar Ubangiji ba ta ƙarewa,Haka kuma jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.

23. Su sababbi ne kowace safiya,Amincinka kuma mai girma ne.

24. Na ce, “Ubangiji shi ne nawa,Saboda haka zan sa zuciya gare shi.”

25. Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke sauraronsa,Da wanda suke nemansa kuma.

Mak 3