Luk 7:13-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Da Ubangiji ya gan ta, ya ji tausayinta, ya kuma ce mata, “Daina kuka.”

14. Sa'an nan ya matso, ya taɓa makarar, masu ɗauka kuma suka tsaya cik. Sai Yesu ya ce, “Samari, na ce maka ka tashi.”

15. Mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuwa ya ba da shi ga uwa tasa.

16. Sai tsoro ya kama su duka, suka ɗaukaka Allah suna cewa, “Lalle, wani annabi mai girma ya bayyana a cikinmu,” da kuma, “Allah ya kula da jama'arsa.”

17. Wannan labarin nasa kuwa ya bazu a dukan ƙasar Yahudiya da kewayenta.

18. Sai almajiran Yahaya suka gaya masa dukan abubuwan nan.

Luk 7