Luk 22:63-66 Littafi Mai Tsarki (HAU)

63. Sai mutanen da suke riƙe da Yesu suka yi ta masa ba'a, suna dūkansa.

64. Suka ɗaure masa idanu, suka tambaye shi, suka ce, “Yi annabci! Wa ya buge ka?”

65. Suka kuma yi ta masa baƙaƙen maganganu masu yawa, suna zaginsa.

66. Da gari ya waye sai majalisar shugabannin jama'a ta haɗu, da manyan firistoci da kuma malaman Attaura. Suka kai shi ɗakin majalisarsu suka ce,

Luk 22