L. Mah 8:16-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Ya kama dattawan garin Sukkot ya hukunta su da ƙayayuwa.

17. Ya kuma rushe hasumiyar Feniyel, ya karkashe mutanen birnin.

18. Sa'an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka kashe a Tabor?”Suka amsa, “Kamar yadda kake, haka suke. Suna kama da 'ya'yan sarki.”

19. Gidiyon ya ce musu, “Su 'yan'uwana ne, mahaifiyarmu ɗaya. Da ba ku kashe su ba, da ba zan kashe ku ba.”

20. Ya ce wa Yeter, ɗan farinsa, “Tashi, ka kashe su.” Amma saurayin bai zare takobinsa ba, gama yana jin tsoro domin shi yaro ne.

L. Mah 8