1. Sai Ubangiji ya yi wa Musa magana a jejin Sinai a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar, ya ce,
2. “Sai Isra'ilawa su kiyaye Idin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokacinsa.
3. A rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, da maraice za su kiyaye shi a ƙayyadadden lokacinsa bisa ga dokokinsa da ka'idodinsa duka.”
4. Musa kuwa ya faɗa wa Isra'ilawa su kiyaye Idin Ƙetarewa.
15-16. A ranar da aka kafa alfarwa ta sujada, sai girgije ya sauko ya rufe ta. Da maraice kuwa girgijen yana kamar wuta.