L. Kid 32:2-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. sai suka je wurin Musa da Ele'azara firist, da shugabannin taron jama'ar,

3. suka ce, “Atarot, da Dibon, da Yazar, da Bet-nimra, da Heshbon, da Eleyale, da Simba, da Nebo, da Ba'al-meyon,

4. ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban taron jama'a, ƙasa ce mai kyau don dabbobi. Ga shi kuwa, barorinka suna da dabbobi da yawa.

5. Idan mun sami tagomashi a gare ka, ka ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu, kada ka kai mu a wancan hayin Urdun.”

6. Amma Musa ya amsa musu ya ce, “Wato sai 'yan'uwanku su yi ta yaƙi,ku kuwa ku yi zamanku a nan, ko?

7. Don me za ku karya zuciyar jama'ar Isra'ila daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?

L. Kid 32