L. Kid 28:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Ubangiji ya umarce Musa,

2. ya dokaci Isra'ilawa su tabbatar cewa sun miƙa wa Allah hadaya ta abinci tare da hadayun da za a yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci bisa ga yadda ake bukata.

3. Waɗannan su ne hadayu na abinci da za a miƙa wa Ubangiji, hadaya ta ƙonawa ta kowace rana, raguna biyu 'yan bana ɗaya ɗaya marasa lahani.

4. A miƙa ɗan rago ɗaya da safe, ɗaya kuma da maraice,

5. da kuma mudun lallausan gari, kwaɓaɓɓe da man zaitun mafi kyau har rubu'in moɗa.

6. Hadaya ce ta ƙonawa kullum, wadda aka kafa a Dutsen Sinai, don daɗin ƙanshi, hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji.

L. Kid 28