1. Sai 'ya'yan Zelofehad, mata, ɗan Hefer ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manassa, ɗan Yusufu, suka tafi ƙofar alfarwa ta sujada. Sunayen 'ya'ya, matan ke nan, Mala, da Nowa, da Hogla, da Milka, da Tirza.
2. Da suka tafi, suka tsaya a gaban Musa da Ele'azara, firist, da gaban shugabanni, da dukan taron jama'a, suka ce,
3. “Mahaifinmu ya rasu cikin jeji. Ba ya cikin ƙungiyar Kora wadda ta tayar wa Ubangiji. Ya rasu saboda alhakin zunubinsa. Ga shi, ba shi da 'ya'ya maza.