10. Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora. Wuta kuma ta cinye sauran mutanen ƙungiyar, mutum ɗari biyu da hamsin suka mutu. Suka zama abin faɗakarwa.
11. Amma 'ya'yan Kora ba su mutu ba.
12. 'Ya'yan Saminu, maza, bisa ga iyalansu, su ne Yemuwel, da Yamin, da Yakin,
13. da Zohar, da Shawul. Waɗannan su ne iyalan kabilar Saminu.
14. Yawansu ya kai mutum dubu ashirin da biyu da ɗari biyu (22,200).
15. Zuriyar Gad bisa ga iyalansu, su ne Zifiyon, da Haggi, da Shuni,
16. da Ezbon, da Eri,
17. da Arodi, da Areli.
18. Waɗannan su ne iyalan kabilar Gad. Yawan mutanensu ya kai dubu arba'in da ɗari biyar (40,500).
19. Kabilar Yahuza ke nan, (Er, da Onan, 'ya'yan Yahuza sun mutu a ƙasar Kan'ana).
20. Sauran 'ya'yansa bisa ga iyalansu su ne, Shela, da Feresa, da Zera,
21. da Hesruna, da Hamul.
22. Waɗannan su ne iyalan kabilar Yahuza. Yawan mutanensu ya kai dubu saba'in da shida da ɗari biyar (76,500).
23. Kabilar Issaka ke nan bisa ga iyalansu, da Tola, da Fuwa,
24. da Yashub, da Shimron.
25. Waɗannan su ne iyalan kabilar Issaka. Yawansu ya kai mutum dubu sittin da huɗu da ɗari uku (64,300).
26. Kabilar Zabaluna ke nan bisa ga iyalansu, Sered, da Elon, da Yaleyel.