L. Kid 13:29-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3-15. Musa kuwa ya yi biyayya, daga jejin Faran ya aika da waɗannan shugabanni,Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ra'ubainu.Shafat ɗan Hori, daga kabilar Saminu.Kalibu ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuza.Igal ɗan Yusufu, daga kabilar Issaka.Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Ifraimu.Falti ɗan Rafu, daga kabilar Biliyaminu.Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zabaluna.Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manassa.Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan.Setur ɗan Maikel, daga kabilar Ashiru.Nabi ɗan Wofsi,daga kabilar Naftali.Geyuwel ɗan Maci,daga kabilar Gad.

29. Amalekawa suna zaune a Negeb, Hittiyawa kuwa, da Yebusiyawa, da Amoriyawa suna zaune a ƙasar tuddai, Kan'aniyawa suna zaune kusa da teku, da kuma kusa da Kogin Urdun.”

30. Amma Kalibu ya sa mutane su yi shiru a gaban Musa, ya ce, “Bari mu tafi nan da nan mu mallaki ƙasar, gama za mu iya cinta.”

31. Sai mutanen da suka tafi tare da shi suka amsa suka ce, “Ba za mu iya haurawa, mu kara da mutanen ba, gama sun fi mu ƙarfi.”

L. Kid 13