L. Kid 12:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Maryamu da Haruna suka zargi Musa saboda mace, Bahabashiya, wadda ya aura.

2. Suka ce, “Da Musa kaɗai ne, Ubangiji ya yi magana, bai yi magana da mu kuma ba?” Ubangiji kuwa ya ji.

3. (Musa dai mai tawali'u ne ƙwarai, fiye da kowane mutum a duniya.)

4. Farat ɗaya sai Ubangijiya ce wa Musa, da Haruna, da Maryamu, “Ku uku, ku tafi zuwa alfarwa ta sujada.” Sai su uku suka tafi.

L. Kid 12