L. Fir 26:8-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Mutum biyar ɗinku za su runtumi mutum ɗari, mutum ɗari ɗinku za su runtumi mutum dubu goma. Maƙiyanku kuwa za su fāɗi a gabanku ta kaifin takobi.

9. Zan dube ku da idon rahama, in sa muku albarka, in riɓaɓɓanya ku. Zan tabbatar muku da alkawarina.

10. Za ku girbi amfani mai yawa har kun zubar da sūnā tukuna kafin ku sami wurin ajiye sabo.

11. Zan kafa wurin zamana a tsakiyarku, ba kuwa zan gaji da ku ba.

12. Zan yi tafiya tare daku, in zama Allahnku, ku kuma ku zama mutanena.

13. Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, don kada ku zama bayinsu. Na karya ikonsu da yake danne ku, na bar ku ku yi tafiya a sake.”

L. Fir 26