27. “Amma idan duk da haka ba ku kasa kunne gare ni ba, amma kuka ci gaba da tayar mini,
28. sai ni ma in tayar muku da fushi, in hukunta ku har riɓi bakwai, saboda zunubanku.
29. Za ku ci naman 'ya'yanku mata da na 'ya'yanku maza.
30. Zan lalatar da masujadanku, in rurrushe bagaden ƙona turarenku, in jefar da gawawwakinku a kan gumakanku, raina kuwa zai ji ƙyamarku.
31. Zan sa biranenku su zama kangwaye, in mai da wuraren yin sujada kufai, ba zan shaƙi ƙanshin turarenku ba.