6. Da yake kun yi na'am da Almasihu Yesu Ubangiji, to, sai ku tsaya a gare shi,
7. kuna kafaffu, kuna ginuwa a cikinsa, kuna tsayawa da bangaskiya gaba gaba, daidai yadda aka koya muku, kuna gode wa Allah a koyaushe.
8. Ku lura fa, kada kowa ya ribace ku ta hanyar iliminsa na yaudarar wofi, bisa ga al'adar mutane kawai, wato, bisa ga al'adun duniyar nan, ba bisa ga koyarwar Almasihu ba.
9. Domin a cikinsa ne cikin jiki dukkan cikar Allahntaka take tabbata.
10. A gare shi ne aka kammala ku, wanda yake shi ne shugaban dukkan sarauta da iko.
11. A cikinsa ne kuma aka yi muku kaciya, ba kuwa yin mutum ba, amma wadda Almasihu ya yi muku ce, ta wurin tuɓe halinku na mutuntaka.
12. An kuma binne ku tare da shi a wajen baftisma, inda kuma aka tashe ku tare da shi saboda bangaskiyarku ga ikon Allah, wanda ya tashe shi daga matattu.