1. To, ina so ku san irin yawan shan faman da nake yi dominku, da waɗanda suke a Lawudikiya, da kuma duk waɗanda ba su taɓa ganina ba.
2. Sona a ƙarfafa musu zuciya, ƙauna tana haɗa su, har su sami dukkan mayalwaciyar fahimta tabbatacciya, da sanin asirin nan na Allah, wato Almasihu,
3. wanda shi ne taska, wato maɓoyar dukkan mafifitan hikima da sani.
4. Na faɗi wannan ne don kada kowa ya hilace ku da maganar yaudara.