K. Mag 30:3-29-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Kada ka kushe bara a wurin maigidansa domin kada ka yi laifin da zai sa a la'ance ka.

11. Akwai waɗansu mutane da sukan zagi iyayensu maza, ba sukan kuma nuna godiya ga iyayensu mata ba.

12. Akwai waɗansu mutanen da suke ganin kansu tsarkaka ne, alhali kuwa ƙazamai ne su.

13. Akwai waɗansu mutane da suke yi wa jama'a ƙallon raini suna ɗaurin gira.

14. Akwai waɗansu mutane waɗanda haƙoransu takuba ne, mataunansu kuma wuƙaƙe ne, don su cinye matalauta da masu fatara daga duniya.

17. Idan ɗa ya raina mahaifi, ya kuma yi wa mahaifiya ba'a hankakin kwari za su ƙwaƙule masa idanu, 'ya'yan mikiya za su cinye.

20. Ga yadda al'amarin mazinaciya yake, takan yi sha'aninta sa'an nan ta yi wanka ta ce, “Ban yi laifin kome ba!”

K. Mag 30