Josh 4:15-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Ubangiji kuma ya ce wa Joshuwa,

16. “Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin shaida, su fito daga cikin Urdun.”

17. Sai Joshuwa ya umarci firistocin su fito daga cikin Urdun.

18. Da firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari na Ubangiji suka fito daga tsakiyar Urdun, suka taka sandararriyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya malalo ya tumbatsa kamar dā.

19. Rana ta goma ga watan ɗaya jama'a suka haye Urdun, suka yi zango a Gilgal a gabashin iyakar Yariko.

20. Joshuwa ya kafa duwatsun nan goma sha biyu da suka ɗauko daga Urdun a Gilgal.

21. Sai ya ce wa Isra'ilawa, “Sa'ad da wata rana 'ya'yanku suka tambayi ubanninsu ma'anar duwatsun nan,

Josh 4