Josh 19:17-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Kuri'a ta huɗu ta faɗo a kan kabilar Issaka bisa ga iyalanta.

18. Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar su ne, Yezreyel, da Kesullot, da Shunem,

19. da Hafarayim, da Shiyon, da Anaharat,

20. da Rabbit, da Kishiyon, da Ebez,

21. da Remet da En-ganim, da En-hadda, da Bet-fazzez.

22. Iyakar kuma ta bi ta Tabor, da Shahazuma, da Bet-shemesh. Sa'an nan ta gangara a Kogin Urdun. Akwai garuruwa goma sha shida da ƙauyukansu.

23. Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke a yankin ƙasar da kabilar Issaka ta gāda bisa ga iyalanta.

24. Kuri'a ta biyar ta fāɗo a kan kabilar Ashiru bisa ga iyalanta.

25. Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar, su ne Helkat, da Hali, da Beten, da Akshaf,

26. da Alammelek, da Amad, da Mishal. A wajen yamma, iyakar ta bi ta Karmel da Shihor-libnat.

27. Daga nan sai ta nausa wajen gabas, ta bi ta Bet-dagon, da Zabaluna, da kwarin Iftahel a wajen arewa zuwa Bet-emek da Nayil. Ta yi gaba a wajen arewa zuwa Kabul,

28. da Hebron, da Rehob, da Hammon, da Kana, har ta bi ta Sidon Babba.

29. Daga can ta nausa zuwa Rama, ta bi ta garun birnin Taya, sai kuma ta nausa zuwa Hosa, sa'an nan ta gangara Bahar Rum, wajen Mahalab, da Akzib,

Josh 19