11. Ubangiji yana sanarwa ga dukan duniya,Cewa, “Ku ce wa jama'ar Urushalima,Ubangiji Mai Cetonku yana zuwa,Yana kawo mutanen da ya cece su.”
12. Za a ce da ku, “Tsattsarkar Jama'ar Allah,”“Jama'ar da Ubangiji ya Fansa!”Za a kira Urushalima, “Birnin da Allah yake Ƙauna,”“Birnin da Allah bai Yashe shi Ba.”