4. Ki duba kewaye da ke, ki ga abin da yake faruwa,Mutanenki suna ta tattaruwa domin su komo gida!'Ya'yanki maza za su taho daga nesa,Za a ɗauki 'ya'yanki mata kamar yara.
5. Za ki ga wannan, ki cika da farin ciki,Za ki yi rawar jiki saboda jin daɗi.Za a kawo miki dukiyar al'ummai,Wato waɗanda suke a ƙasashen hayi.
6. Babban ayarin raƙuma zai zo daga Madayana da Efa.Za su zo daga Sheba, su kawo zinariya da kayan ƙanshi.Mutane za su ba da labari mai daɗi a kan abin da Allah ya yi!
7. Dukan tumaki na Kedar da Nebayot,Za a kawo miki su hadaya,A kuwa miƙa su a kan bagade domin Ubangiji ya ji daɗi.Ubangiji zai darajanta Haikalinsa fiye da dā.
8. Waɗannan jiragen ruwa fa? Suna tafe kamar gizagizai,Kamar kurciyoyi suna komowa gida.