Ish 49:17-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. “Su waɗanda za su sāke gina ki suna tafe yanzu,Waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su tashi.

18. Ki dudduba, ki ɗaga idonki, ki ga abin da yake faruwa!Mutanenki suna tattaruwa suna komowa gida!Hakika, da yake ni ne Allah Mai Rai,Za ki yi fāriya da mutanenki,Kamar yadda amarya take fāriya da kayan adonta!

19. “Aka lalatar da ƙasar, ta zama kufai,Amma yanzu za ta yi wa waɗanda suke komowa domin su zauna cikinta kaɗan.Waɗanda suka lalatar da ke kuwa,Za a kawar da su daga gare ki.

Ish 49